Posts

Showing posts from December, 2021

MALIKUSSAIFI IBN ZIYYAZANUN LITTAFI NA DAYA-06

Image
Fassarar Aliyu Abubakar Sharfadi . Ya dubi Sarki Afarahu ya ce Shikenan ga abin da muke gudu nan ka jawo mana. Koda sarki Afarahu ya ji abin da boka ya ce akan maganar da Washilfala ya faɗa sai ya ji tsoron kada bokan nan ya je ya shirya masa wani makircin a wajen babban sarki, sai ya yi dabara ya ce da Washilfala ai wannan ba wani abinda zaka damu kanka ba ne, domin kuwa kaine kafi cancanta da ka aureta, kodan kuɓutar da ita da kayi daga hannun wannan baƙin aljanin Muftaɗihu, na riƙeka ɗane a wajena, ita kuma Shamatu na wakilta boka Saƙaradiyyuna ya zamo waliyinta, saboda haka yanzu a wajensa zamu nemi auren. Koda boka Saƙaradiyyuna ya ji an damƙa ragamar aure a hannunsa sai ya yi murmushi yana rayawa a zuciyarsa ya samu hanya mai sauki ta halaka Washilfala. Sarki Afarahu ya dubi boka Saƙaradiyyuna ya ce Yaro yana neman auren yarinya mene ne dukiyar aurenta? Boka ya yi dariya ya ce Kasan neman auren ƴaƴan sarakuna ƙasaitattu irinka yana da tsada sosai, to mu yanzu ba dinare, azurfa ...

Hikayoyin kaifafa zukata

Image
IMANI SHINE TABBATAR AIKI Rubutu; Adam Muktar An yi wani malami da almajirinsa . Banda karatu dayake dauka a wajen malamin har yakan tambaye shi nakulkula.A cikin irin haka ne har yabawa almajirin wata addu,a wadda in an karanta ta ana iya taka ruwa a wuce. Ana cikin haka sai tafiya ta kama malamin zuwa wani dan kauye. A daren tafiyar anyi ruwa kwazari har korama ta kawa. Da suka iso koramar sa almajiri yace "Yau ga ranar addu,a " sai ya karanta ya taka ruwa caf-caf-caf ya haye.Malami ya karanta ya taka sai tsulum ya tsunduma . Ya nanata amma a banza sai yaro ya takayo ya dawo .Malami ya karanta dai dai da yaro amma ya tsulluma , yaro kuwa ya haye .Malami ya gigice ya ga ya ya haka. Can sai yaro yace" malam naga s duk inda kuskuren yake.Na ga kai in ka karanta sai ka ja wondonka sama .Ni kuma ai ko wannan tunanin ba bana yi balle in ja wandona. Tunda aka ce a taka a wuce , yaya kuma za,a yi tunanin jikewa

Gabatarwa

Image
HIKAYOYIN KAIFAFA ZUKATA NA MALAM AMINU KANO Assalamu alaikum warahhamatullahi ta,ala wabarakatuhu.Bayan haka kamar yadda muka sani a kowane zamani a ko'ina a duniya za a ga koyaushe mutane suna da hanyoyin koyar da ya'yansu hankali tsinkaya da basira jurewa hakuri azanci da dabara da dai sauran halayen da za su taimake su lokacin da za su fara ma'amalantar mutanen zamani. Daya daga cikin hanyoyin nan yakan kasance iya amfani da harshe wajen magana.Daga nan sai labarai na gaske dana almara,zaurance,karin magana,azancin tatsuniya,habaici,wa,azi,waka,cita cita da sauransu. Harshen hausa ko kadan bai gaza ba wajen wadan nan ba.haka nan kuma wajen labaran ban dariya,azanci,tausayi,wayo da dabara. Ganin abbubban nan sun fara bacewa a kasar nan,da kuma ganin rashinsu zai tauye mana wata daraja nan gaba balle ga bada ilimi kyauta ga ya'yanmu yazo, na dauki nauyin rubuta wannan dan littafi da fatan taimakawa a wannan siffa.kuma ina kara fata da addu,a cewa zai zama...

MALIKUSSAIFI LITTAFI NA DAYA 05

Image
Malikussafi ibn Ziyyazanu na daya - 05 Tsohon ya amsa da cewa ita wannan bulala idan aka daki aljani da ita konewa yake a take ya mutu, saboda haka duk wanda ya mallaketa to zai mallaki Aljanun duniya. Washilfala ya ce da tsohon to ina bulalar take, tsoho ya shiga da Malukussaif cikin kogon ya nuna masa bulala, koda yaga bulalar sai ya ce da da tsohon to ɗaukota mu gani, tsoho ya ce a'a ai bani da iko zuwa kusa da ita sai dai kai. Washilfala ya miƙa hannun ya ɗauko wannan bulala, koda tsohon nan yaga haka sai ya yi niyyar ya yi masa wayo ya ce, Bani na gani Sai Washilfala ya ce A'a bazan baka ba sai ka fitar da ni, kuma ka sani a hanyar zuwa garin Duwar. Da tsoho ya ji haka sai ya ɗaukoshi ya kawoshi kusa da garin Duwar ya ajiye shi, ya kuma nuna masa hanyar da zai bi ya shiga garin. Koda wannan tsohon ya sauke Washilfala sai ya raya a zuciyarsa ya ce Tunda wannan tsohon yace shi aljani ne bari na gwada akansa na gani in da gaske ne, sai ya daddage ya tsula wa wannan aljani...

MALIKUSSAIFI LITTAFI NA DAYA 04

MALIKUSSAIF IBN ZAYYAZANUN -04 A lokacin da Wahshilfala ya kai shekara bakwai, sai ya buƙaci yana son ya fara hawa doki. Sarki ya sa aka ɗauko masa wani ɗan ƙaramin doki. Da Wahshilfala yaga wannan dokin sai ya rainashi ya ce, “Shi bazai hau wannan ƙaramin dokin ba, shi babba ya ke so. Sarki yasa aka mayar da wannan dokin aka kawo masa wani baƙin ingarman doki mai digo-digon fari a wuyansa da kirjinsa. Wahshilfala yace wannan doki yayi masa, yayi tsalle ya ɗare kansa ya yi sukuwa a gaban jama'a yana dawowa gaban sarki yana tirjiya. Daga nan Wahshilfala ya fara koyon yaƙi da takobi kuma cikin ƙanƙanin lokaci ya kware a harkar faɗa da takobi ya zamana kaf yaran dake sa'anninsa bawanda zai iya ja da shi har manyan ma. Ganin haka yasa Sarki Afarahu ya dinga alfahari da shi, kuma ya ware masa masu yimasa hidima. Wata rana sarki yana zaune a fadarsa da 'yan Majalisar sa ana fadanci can sai ga bokan Babban Sarki mai suna Saƙaradiyyuna ya shigo faɗar sarki da yan majalisa suka mi...

MALIKUSSAIFI LITTAFI NA DAYA 03

Image
Malikussafi ibn Ziyyazanu na daya - 03 Shi wannan mutumin, mutumin ƙasar Duwar ne, kuma ita wannan masarauta ta kasance ta na ƙarƙashin Ƙasar Habasha ne. Da Isar wannan Maharbi gida tun daga waje ya Fara kwala wa matarshi Kira harya shiga cikin gidan. Da isar shi ya miƙa mata yaron, kana ya sakko da akwatun da yake a kansa, sannan ya kwashe labari kaf! Ya bata. Ya ce, "Kinga shikenan daman bamu taɓa haihuwa ba ga shi Allah ya bamu ɗa, sannan kuma ga dukiya Allah ya bamu." Da matar ta ji haka sai ta ce "Haba! Mai gida kai ka dubi irin wannan kyakkyawan yaron, da ganinsa kasan dan sarakuna ne, ko kuma manyan attajirai ta ya ya zamu iya rikeshi? Kuma kaga shi farine muko duk baƙaƙe ne, ai ana gani za a ce sato shi muka yi aje a samu a cikin wani hali, kawai yanzu ka daukeshi kaje ka kai wa Sarki shi domin wannan yaro yafi karfin mu." Da mijin ya ji haka sai ya zauna ya yi tunani, kuma sai ya aminta da shawarar matar ta shi. Saboda haka sai ya kinkimi akwatun sannan y...

MALIKUSSAIFI LITTAFI NA DAYA 02

Image
Fassarar Aliyu Abubakar Shafadi Waziri ya bashi takarda wannan ya suƙwani doki ya bi ta wata ɓarauniyar hanya ya nufi Hamra'u Yemen cikin dare ba tare da kowa ya ganshi ba. Bayan kwana uku sai aka yi Sa'a wannan bawa na waziri Baharu ya riga ƴan aiken sarki Saifu zuwa Hamra'u Yemen. Da zuwan sa cikin hanzari ya isa fada aka yi masa iso gurin Sarki, da shigarsa ya faɗi ya yi gaisuwa sannan ya miƙa wannan takarda ga Sarki Ziyyazinun, ya umarci Sarki da a sallameshi da wuri, domin kada ƴan aiken Sarki Saifu su iso su taradda shi suyi tsammanin wani abu ne. Nan Sarki ya yi masa ƙaututtuka sannan ya sallameshi, shi kuma ya kama hanyar sa ta komawa birnin Habasha. Bayan kamar sa'a uku da tafyar bawan nan sai ga ƴan aiken Sarki Saifu sun iso wannan birnin. Da zuwansu suma sai suka wuce fada aka yi masu iso suka shiga sannan suka yi gaisuwa gaban Sarki, kuma suka isar da saƙonsu Sarki Saifu na ƙyautar Ƙamriyya da Sarkisu Sarki Saifu ya ba wa Sarki Ziyyazinun. Koda Sarki Ziyyaz...

MALIKUSSAIFI LITTAFI NA DAYA

Image
Fassarar Aliyu Abubakar Sharfadi Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin Sarki da manzonSa Annabinmu Muhammad, tsira da amincin Allah Su ƙara tabbata a gareshi, wanda ya bamu iko ga jama'a domin su samu abin ɗebe kewa da nishadantarwa yayin karantashi. Shi wannan littafin, fassarace daga harshen larabci zuwa na hausa domin jama'a Su amfaneshi. Shi wannan littafi mafi yawancin mutanen yanzu basu sanshi ba, domin Malamai ne ada suke karanta wa jama' a shi idan suna jin nishadi. Zaku ji cewa Wannan littafin ya kunshi labaran soyayyaya, nishadi da kuma abubuwa iri daban-daban, wadanda suka kunshi sha'anin bokanci da tsafe-tsafe wanda mutanen wancann lokaci suka kware a kai. Za kuma aji yadda rayuwa take kasancewa ga wannan sarki, tun tasowar sa da kuma girmansa, kama izuwa lokacin daya zama kasaitaccen Sarki da kuma mutuwar sa. Kuma za aji cewa wannan littafin ya shafi ɓangaren addini da kuma ma'amaloli na rayuwar al'umma. Malukussaif Ibn Ziyyazinun a karan kansa a...

Waken Suya

Image
YADDA A KE NOMAN WAKEN SUYA Wace kasa waken suya yake bukata? waken suya yana bukatar kasa wacce take Ita ba tabo ba bakuma yashi ba wannan kasar Ita waken suya yafi bukata amma Ana yi a yashi da tabon amma gaskiya bai fiya bada abunda ake so ba sannan sai a haro da huda. Yaushe ake shukar waken suya? Ana shuka waken suya ne bayan an tabbatar ruwa ya tsaya bawai anayin ruwan farko ko na biyu kaje kai shikaba sai ruwa ya tsaya sannan sai ka shuka saboda idan ba laima a tare dashi har ya kwanta to baya tashi sai dai ka sake shuka wani idan zakai shukar anasa 3 zuwa 4 a rami daya sannan bayan kwana 10 zakazo kai kwafi ma'a duk inda bata fitoba kasake shukawa. Sannan bayan sati 1 zuwa kwana 10 sai ai noma sannan sai ka barshi har sai lokacin da ya fara fure sai azo ai huda. Shin waken suya yana bukatar taki? Waken suya baya bukatar taki mutukar ka zuba takin gargajiya a farko kafin a karce wajan baka bukartar zuba wani taki saboda yana samarwa kansa taki da kasa. Yaus...

Gobe Jar Kasa 01

Gobe jar kasa LITTAFIN SHAFI'U DAUDA GIWA . TANA a zaune akan katifarta ita kadai a cikin dan karamin dakinta ta dade a haka tun kusan kimanin awa daya tana kallon kundin adana hotunanta (album) wanda ta rikeshi da hannuwanta biyu kamar littafin karatu Duk da yake ta rufe kofar dakin nata hakan bai hanata ganin hotunan ba ta hanyar hasken kwan wutar dake goshin dakin wutar babu karfi wani lokacin ayi kamar za'a dauketa zuwa can kuma sai ta tsaya batayi mamakin haka ba don kuwa ruwa aketa shekawa a daidai lokacin kamar da bakin kwarya ga kuma iska da walkiya don haka za'a iya dauke wutar akowane lokaci bayan yanzu Duk lokacin da akace ana ruwa indai wannan budurwar tana gida sau da yawa babu abinda tafi sha'awa irin ta dauko hotunanta na da Dana yanzu ta rika kallonsu tana tunanin abubuwan da suka gabata a rayuwarta A haka zata wuni a cikin dakin nata har zuwa lokacin da za'a dauke ruwan Idan ta gaji saita fito waje tasha iska ko kuma taje dakin mahaifiyarta suyi hi...

GABATARWA TA BIYU

GODIYA Da sunan Allah mai rahama mai jin kai, dukkan yabo da godiya sun tabbata a gare shi sarkin da ya yi sammai da kassai. Salati da gaisuwa ga shugaban hallittu annabi muhammadu ( s.a.w). Na sadaukar da wannan shafi ga mahaifiya ta. Allah ya jikan ta da rahama.

Gabatarwa Ta Daya

MARAINIYA Shafin Hausa na farko wanda zai rika kawo muku abubuwan da suke faruwa a kasar Hausa. Haka kuma a gefe guda shafin ya samu tagomashi ta bangaren marubuta labaru na Hausa don makaranta masu bukatar abin debe kewa da nishadantuwa.